
Sanata Natasha Akpoti ta koka da cewa, tana cikin fargabar tsaro.
Sanata Natasha ta bayyana bakane a majalisar dinkin Duniya inda aka yi zama na mata ‘yan majalisa a Birnin New York City na kasar Amurka.
Bayan data gabatar da korafi kan dakatar da ita da aka yi daga ayyukan majalisar Najeriya, Sanata Natasha Akpoti tace tana fargaba kan tsaron kanta.
Tace za’a iya kamata a tsare ba bisa son ranta ba a birnin New York City na kasar Amurka inda tace kuma tana zargin Gwamnatin Najeriya da hannu game da hakan.