Monday, September 7
Shadow

An yi gàrkùwà da soja da wasu sauran mutane a Abuja

Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja na cewa an yi garkuwa da wata sojar ruwa dake aiki a hedikwatar tsaro ta kasa tare da wasu mutane.

Lamarin ya farune a Mpape dake Abuja ranar Juma’a inda aka shiga har gida aka tafi da wadanda aka yi garkuwar dasu.

Wata majiya ta shaida cewa, wadanda aka yi garkuwa dasu din an kira iyalansu inda ake neman Naira Miliyan 100 a matsayin kudin Fansa.

Jimullar mutane 3 ne aka yi garkuwar dasu, ciki hadda sojar me suna Lt. Cynthia Akor.

Hukumomin soja dai basu ce uffan kan lamarin ba.

Karanta Wannan  TIRƘASHI: Na Tsani Katsalaɲdan A Rayuwata, Døn Haka Babu Wanda Ya Isa Ya Hana Ni Buɗe Gashin Kaina, Saboda Ni Yin Magana Ne Ma Ke Sa Na Yi Abu, Koda Abinda Na Yi Ba Mai Kyau Ba Ne, Muddin Za A Ce Na Daina Ni Kuma A Wannan Lokacin Ne Ma Zan Fara, Inji Jarumar Finafainan Hausa, Nafisat Abdullahi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *