Mazauna wani waje a kusa da garin Jere na Jihar Kaduna sun sha mamaki bayan da aka ga wani farin abu mai kama da gajimare ya bayyana. Bidiyoyin da suka bazu a kafafen sada zumunta sun nuna yadda mutane ke kallon lamarin cikin mamaki da al’ajabi. Sai dai har yanzu ba a tabbatar da ainihin abin da ya haddasa wannan lamari ba, ko ya faɗo ne daga sama ko kuma ya fito ne daga ƙasa.
Mazauna wani waje a kusa da garin Jere na Jihar Kaduna sun sha mamaki bayan da aka ga wani farin abu mai kama da gajimare ya bayyana. Bidiyoyin da suka bazu a kafafen sada zumunta sun nuna yadda mutane ke kallon lamarin cikin mamaki da al’ajabi. Sai dai har yanzu ba a tabbatar da ainihin abin da ya haddasa wannan lamari ba, ko ya faɗo ne daga sama ko kuma ya fito ne daga ƙasa.