Saturday, January 24
Shadow

Babu Gwamnatin Data Samu Nasara da Muka samu a shekaru biyu da suka gabata a tarihin Najeriya>>Tinubu

Ministan Yada labarai, Muhammad Idris ya bayyana cewa, babu Gwamnatin data samu nasarar da Gwamnatin Tinubu ta samu a shekaru 2 da suka yi suna mulki.

Ya bayyana hakanne a Abuja wajan wani taron karawa juna Sani kan harkar tsaro da wayar da kan ‘yan kasa.

Yace babu gwamnatin data samu nasarar da Gwamnatin Tinubu ta samu a shekaru biyu da suka gabata, da farko dai ya yi maganin masu ci da tallafin man fetur.

Da kuma masu almundahana a harkar canjin Kudi, Ga kuma bashin karatu da yake baiwa dalibai, ga gina Tintuna da sauransu.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas Ya Janye Kudirin Tilasta Zaɓe wanda za'a rika cin mutum tarar Naira dubu dari bayan da ya sha suka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *