Friday, December 5
Shadow

A yayin da Kungiyar Dattawan Yarbawa ta Afenifere take kiran a tsige Shugaba Tinubu saboda bai tsinanawa ‘yan Najeriya komai ba, Kungiyar Matasan Yarbawan sun ce basu yadda a tsige shugaban ba

Kungiyar Matasan Yarbawa, (YYSA) tace bata amince da kiran da kungiyar dattawan Yarbawan ta yi ba na cewa a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda yaudarar ‘yan Najeriya.

Shugaban kungiyar, Olalekan Hammed ne ya fitar da sanarwar ranar Lahadi inda yace zargin da akewa shugaba Tinubu na baiwa kamfanin Mr. Gilbert Chagoury aikin gina titin Legas zuwa Calabar wanda ke da alaka dashi ba gaskiya bane.

Yace kamfanin na da tarihin yin ayyuka masu kyau.

Yace kiran a tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cike yake da siyasa sannan zargin da ake masa bashi da tushe ballantana makama.

Sannan yacw shi Tinubu yana duba cancanta ne kamin ya bayar da aiki.

Karanta Wannan  Dan majalisar Amurka ya zargi Kwankwaso da hannu wajan Mhuzgunawa Kiristoci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *