Friday, December 5
Shadow

Jirgi ko daya marar matuki da kasar Iran ta jefawa Israyla bai kai kasar Israylan ba, Kasashen, Saudi Arabia, Jordan, Qatar, Turkiyya, UAE duk sun tare su

Rahotanni daga gabas ta tsakiya na cewa kasashen Larabawa na cikin wadanda suka tare jirage marasa matuka 100 da kasar Iran ta jefawa Israyla a matsayin martani.

Kasashen Larabawan da suka tare wadannan makamai sun hada da Saudi Arabia, Jordan, Qatar, Turkiyya, UAE.

Sannan kuma akwai kasar Azerbaijan, da Israyla, da Amurka, da Ingila.

Rahotanni sun ce sai da Israyla ta kwace iko da dukkanin sararin samaniyar kasar Iran tana cin karanta babu babbaka da jiragen yakinta.

Karanta Wannan  Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya cika shekaru 68 a yau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *