Friday, December 5
Shadow

Tonon Silili: Ji yanda shugaba Tinubu ya tafi neman lafiya a asirce dan kada ‘yan Najeriya su mai surutu

Rahotanni sun ce tafiyar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi zuwa kasar Saint Lucia da fadar shugaban kasar tace hanyace ta kulla alaka tsakanin kasashen biyu, dabara ce kawai ta neman lafiya da shugaban kasar ya fita yi.

Rahoton yace Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi amfani da kasar Saint Lucia ne dan neman magani inda maimakon a baya da yake zuwa asibiti, a wannan karin likitocin sa ne za’a dakko su dubashi a kasar.

Rahoton wanda ya fito daga Sahara reporters wadda ita kuma tace ta samoshi ne daga wata majiya me tushe ta kusa da shugaban kasar tace, an yi hakanne dan kaucewa idon ‘yan jarida kada su kwarmata cewa shugaban kasar ya je nema lafiyane.

Karanta Wannan  Ku daure ku sake zaben Tinubu a 2027 ko dan ya kammala ayyukan ci gaban da ya faro a Arewa>>Femi Gbajabiamila shugaban ma'aikatan fadar Tinubu ya roki 'yan Arewa

A baya dai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya je neman lafiya kasashen waje wanda hakan yaci karo da suka daga ‘yan Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *