Friday, July 17
Shadow

Da Duminsa: Ji Wata magana da Kwankwaso yayi da zata jawo a kamashi a Bincikeshi

Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA sun ce zasu aikawa da hukumar ‘yansandan Najeriya da sauran jami’an tsaro korafi dan a biciki tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso kan wani ikirari da yayi.

Kungiyar ta bayyana hakane bayan zaman kwamitin zartarwasta, watau NEC

Sakataren kungiyar ta NBA, Etaba Agbor ne ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Maganar da ake zargin Kwankwaso da yi shine, yace a shakerar 2019 ya dauki Abba Kabir Yusuf zuwa ganin alkalan kotun koli ta Najeriya bayan da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta bayyana zaben Kano a matsayin Inconclusive, watau wanda bai kammalu ba.

Karanta Wannan  Dodar Ta tabbata, Kowa ya shaida mulkin Adalci na Shugaba Tinubu dan haka 2027 zai zarce>>Ganduje

A karshe dai kotun kolin ta tabbatarwa da Gwanduje a wancan lokacin cewa shine yaci zaben.

Wannan magana ta tayar da hankuka musamman tsakanin Lauyoyin Najeriya inda suka ce hakan kamar batawa alkalai sunane da nuna cewa an sasu sun aikata abinda ba bisa doka ba.

Lauyoyin sukace wannan abin zai iya sa ‘yan Najeriya su daina ganin Alkalai ko kotu da daraja a rika tunanin wasu manyan mutane na juyasu.

Dan haka ne kungiyarsu ta Lauyoyin suka yanke shawarar mikawa hukumar ‘yansanda da sauran jami’an tsaro korafi a hukumance dan a binciki wadannan kalamai na Kwankwaso.

Idan ba gaskiya bane a karyatasu, idan kuma gasiyane a hukuntashi da sauran wadanda ke da hannu a lamarin.

Karanta Wannan  Tinubu ya bai wa jihohi naira biliyan 108bn kan ambaliya da zaizayar Ć™asa - Shettima

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *