Friday, December 5
Shadow

ABIN FARIN CIKI: Jami’ar Musulunci Ta Madina Ta Ayyana Littafin Prof. Muhd Sani Umar R/Lemo A Kololuwar Mataki

Daga Khalid Yusuf Sambo

Kamar yadda a ke ganin a hoton da ke kasa, shahararriyar Jami’ar nan ta Musulunci ta Duniya da ke Birnin Madinar Manzon Allah (S.A.W) ta ayyana Littafin:

ضوابط الجرح والتعديل عند الحافظ الذهبي

Wallafar Prof. Muhd Sani Umar R/lemo (Hafizahullah) a cikin jerangiyar littafan da za ta yi wa daliban da ke gurbin karatun Digiri na uku (Ph.D) Jarrabawa a cikinsa. Shi ne Littafi daya tilo na mutumin yankin kaf Afirka da ya samu wannan tagomaci.

Hakika wannan yana sake nuna karbuwar Littafin da ficensa a Duniyar ilimi. Da ma kuma Littafi ne da ba a shaida kamarsa a bangarensa ba. Littafin shi ne kundinsa na samun shaidar kammala matakin Digiri na biyu a Jami’ar Musulunci ta Madina, wanda a lokacin ya rabauta na samun koluluwar mataki da jinjina mafi girma a fanninsa.

Karanta Wannan  Mun samar da tsaro sosai a Yankin Arewa, yanzu mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu, sun koma garuruwansu>>Inji Shugaba Tinubu

Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allah Ya kara wa wannan Babban Malami Lafiya da Albarka Allah Ya jikan mahaifansa Ya saka masa da Alkhairi.

Mai Rubutu:
Musa Muhammad Dankwano.
Sakataren Kwamitin Ilimi Na Dr. Muhd Sani Umar R/lemo.
23-02-2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *