Tuesday, May 19
Shadow

Jihar Kebbi ta gano karin ma’adanan karkashin kasa a jihar

Jihar Kebbi ta gabo karin ma’adanai na karkashin kasa a jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Yakubu Ahmed-BK ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.

Yace an gano karin ma’adanan ne a Jega, Dandi, Gwandu, Suru, Birnin Kebbi, Argungu da sauransu.

Wannan na zuwane a yayin da jihar Kebbi ke da ma’adanai kamar su gwal da sauransu.

Ya bayyana gano wadannan karin ma’adanai da cewa, wata hanyace ta karin samun kudin shiga ga jihar.

Karanta Wannan  Babu ruwan mu da ta Halal ko ta Haram ka samu kudin shiga, Kowa, hadda Kharuwaiy sai sun fara biyan Haraji nan da shekarar 2026>>Inji Gwamnatin Tarayya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *