Friday, December 5
Shadow

Da Duminsa: Jam’iyyar NNPP ta Lashe zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono

Jam’iyyar NNPP ta Lashe zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono da aka gudanar jiya, Asabar a Kano.

Da yake bayyana sakamakon zaben da misalin karfe  12:36am na safe, Professor Hassan Shitu ya bayyana dan takarar NNPP, Dr Ali Kiyawa a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 16,198 inda ya kayar da dan takarar APC, Ahmad Kadamu, da ya samu kuri’u 5,347.

‘Yan Jam’iyyar NNPP sun gudanar da zaman dirshan a ofishin INEC inda suka zargi cewa, ana shirin yin murdiyar zabe a sakamakon mazabar Ghari/Tsanyawa.

Kakakin Gwamnatin jihar Kano, Sanusi Tofa yace ba zasu bar kofar INEC din ba sai an fadi sakamakon Ghari/Tsanyawa

Karanta Wannan  Kaso 80 na masu ilimin Najeriya kiristocine, hakanan kaso 85 na masu juya tattalin arzikin Kasarnan Kirista ne

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *