Thursday, February 5
Shadow

Dangote na sayarwa da kasashen waje mai a farashi me sauki fiye da Najeriya>>’Yan kasuwar mai suka koka

‘Yan kasuwar man fetur sun koka da cewa, Dangote na sayarwa da kasashen waje man fetur a farashi me sauki fiye ye da yanda yake sayarwa a Najeriya.

”Yan kasuwar sun ce ‘yan kasar waje na samun ragin kusan Naira 65 akan kowace Lita idan aka kwatanta da farashin man da Dangoten ke sayarwa a Najeriya.

Dan hakane ma suka ce wani lokacin basa saye a wajan Dangote sai su je wajan ‘yan kasar wajen da ya sayarwa su saya a hannunsu su shigo dashi Najeriya.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar DAPPMAN, Olufemi Adewole ne ya bayyana haka ga manema labarai na Punchng.

Yace abinda suke nema a wajan Dangote shine ya rika musu sauki dan haka sai su daina shigo da man daga kasashen waje suna saye a hannunshi.

Karanta Wannan  Jigo a Jam'iyyar PDP, Segun Sowunmi yace a shirye yake ya koma APC duk da a baya ya soki jam'iyyar

Yace Dangote da gangan yake karya farashin mai da zarar ya ga sun kawo mai daga gasashen waje.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *