Friday, December 5
Shadow

Gwamnonin Arewa sun nemi Shugaba Tinubu ya haramta ayyukan hakar ma’adanai

Gwamnonin Arewa sun nemi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da ayyukan hakar ma’adanai na akalla watanni 6.

Sun ce harkar ma’adanai na taimakawa kara tabarbarewar harkar tsaro a yankin Arewa.

Gwamnonin sun kuma sha alwashin tara N228bn dan magance matsalar tsaro a yankin.

Kowace jiha da kananan hukumomin ta zasu samar da Naira Biliyan 1 inda a hakane za’a tara kudaden.

Hakanan sun goyi bayan samar da ‘yansandan jihohi.

Karanta Wannan  Ki kiyayi kanki ki janye zargin da kikewa dan mu in ba haka ba wallahi zamu durkusa mu gayawa Allah ya mana maganinki>>Matan Inyamurai dana Niger Delta suka gargadi Sanata Natasha Akpoti

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *