
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikewa da kotun Magistrate dake Abuja da korafin cewa, ana kokarin take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa.
ElRufai yayi zargin cewa, shugaban Hukumar ICPC din Musa Adamu Aliyu ta hannun wasu yaransa ya bayyana masa cewa sharadin sakinsa shine sai idan ya amince zai daina shiga harkar siyasa.
El-Rufai ta hannun Lauyansa yace wannan kokarine na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa wanda ba zai lamunta ba.
Zuwa yanzu dai Hukumar ta ICPC bata ce uffan ba kan zargin da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya mata.