Tuesday, August 25
Shadow

A karshe dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana ranar da zara gyara wutar lantarkin Arewa

Kamfanin TCN ya bayyana ranar Lahadi, 3 ga watan Nuwamba a matsayin ranar da zai gyara wutar lantarkin Arewa.

Kamfanin yace yana yin dukkan mai yiyuwa dan ganin ya dawo da wutar zuwa yankin Arewa.

Wakilin Kamfanin, Sule Abdulaziz ne ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a babban birnin tarayya, Abuja ranar Talata.

Tun ranar 22 ga watan October ne dai aka fara samun matsalar wutar.

Ya kara da cewa suna kokarin dawo da wutar ne bisa kokarin basu tsaro da sojojin Najeriya ke yi.

Karanta Wannan  Duk da tallafin Gwamnatin tarayya, Farashin kayan abincin da ake shigowa dasu daga kasashen yayi tashin gwauron zabi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *