Friday, December 5
Shadow

Da Duminsa: Tinubu ya ba da umarnin sakin yaran da aka gurfanar a kotu kan zanga-zanga

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin sakin dukkan ƙananan yaran da aka kama da zargin cin amanar ƙasa sakamakon shiga zanga-zanga kan tsadar rayuwa.

Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ya ce an kuma kafa wani kwamati da zai bincika yadda aka kama su da sauran lamurransu.

“Shugaban ƙasa ya ce a sake su kuma a sadar da su ga iyayensu,” in ji ministan lokacin da yake magana manema labarai a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Bayanan sun fito ne jim kaɗan bayan kammala rantsar da sababbin ministoci bakwai da Shugaba Tinubu ya naɗa a fadarsa a yau Litinin.

Kwamatin da zai yi aikin zai kasance ƙarƙshin ma’aikatar agaji da rage talauci, in ji ministan.

Karanta Wannan  Ni gadon Musulunci na yi wajan iyayena, amma matata Fasto ce kuma ban taba ce mata ta zama Musulma ba>>Inji Shugaba Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *