![](https://hutudole.com/wp-content/uploads/2025/01/5b0856a6-51d8-4f87-98cc-3c6d5bde508f.jpg.webp)
Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya ta ayyana yau Laraba 1 ga watan Janairu a matsayin 1 ga watan Rajab na shekarar Hijira ta 1446.
Wata sanarwa da Wazirin Sokoto Farfesa Sambo Wali ya fitar a daren da ya gabata ta ce Sarkin Musulmi Sa’ad Abubukar III ne ya bayyana hakan bayan ganin jaririn watan.
Rajab shi ne wata na bakwai a kalandar Musulunci, wanda Hausawa ke yi wa laƙabi da watan Azumin Tsofaffi.