Friday, December 5
Shadow

A wannan shekarar kowa zai ga amfanin gyare-gyaren da gwamnatina ta yi, za’a ji dadi>>Gwamnatin Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, a wannan shekarar da muke ciki ne za’a fara shaida romon gyare-gyaren da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu ta yi.

Wasu daga cikin gyare-gyaren da Gwamnatin ta yi sun hada da cire tallafin man fetur, kara kudin wutar lantarki, kara kudin kira dana data, wanda wadannan abubuwa sun jefa ‘yan Najeriya cikin matsi.

Saidai da yake magana kan lamarin, Ministan yada labarai, Muhammad Idris ya bayyana cewa a wannan shekarar da muke ciki za’a fara ganin amfanin wadannan gyare-gyaren.

Ya bayar da misali da kasafin kudin shekarar 2025 na Naira Tiriliyan 54.2 wanda yace tun da ake a kasarnan ba’a taba yin kamarsa ba.

Karanta Wannan  Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Yace wannan kasafin kudi an tsarashine dan kawowa ‘yan Najeriya ci gaba da saukin rayuwa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *