Monday, April 27
Shadow

Da Duminsa: Kotu ta dakatar da Yunkurin ladaftar da sanata Natasha Akpoti da majalisa ke shirin yi

Babbar kotun tarayya dake Abuja ta dakatar da yunkurin ladaftar da Sanata Natasha Akpoti da majalisar tarayya ke shirin yi.

Lauyoyin Sanata Natasha Akpoti ne suka shigar da kara inda suke neman kotun ta dakatar da kwamitin ladaftarwa dake neman tuhumar sanata Natasha Akpoti.

Mai Shari’a Justice Obiora Egwuatu ya amince da wannan bukata inda yace an dakatar da wannan bincike.

Yanzi dai majalisar ba zata iya ci gaba da binciken sana Natasha Akpoti ba har sai idan an samu daukaka kara ko wani sabon hukuncin ya fito.

Karanta Wannan  Kabir Gombe Kazami ne, Kuma kwanannan shi da Sheikh Bala Lau suka kwacewa marayu makaranta a Gombe, aikinsu kenan zalintar marayu, Sheikh Musa Salihu Alburham da Wani malamin Izalan Jos suka soki Shugabancin Izala na kasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *