Sunday, June 1
Shadow

A yayin da Ake ci gaba da samun hare-haren ‘yan Bìndìgà, Gwnnatin Tarayya tace canjawa tubabbun ‘yan Bìndìgàr ra’ayi da mayar dasu cikin jama’a na da matukar muhimmanci wajan kawo zama Lafiya a kasarnan

Shugaban Hukumar OSC, shirin Gwamnatin tarayya dake kula da canjawa tubabbun ‘yan Bindiga ra’ayi da mayar dasu cikin mutane da koya musu sana’a da basu jari, Yusuf Ali ya kaiwa hukumar NOA ziyara a hedikwatar ta dake Abuja.

Ya kai ziyarar ne ranar 2 ga wata Mayu inda shugaban hukumar ta NOA Lanre Issa-Onilu ya karbeshi, sannan kuma ya bayyana damuwa game da rashin fahimtar wannan shiri da mutane ke yi da yada labaran karya game da shirin.

Saidai shima Lanre Issa-Onilu yace a baya yana da shakku akan wannan shiri da yi masa wani irin kallo amma yanzu ya fahimci abina shirin ya kunsa.

Karanta Wannan  Karuwanci ya kaita jihar Legas>>Hadimin Shugaban kasa ya zargi matashiya 'yar Bautar kasa data soki Shugaba Tinubu

Ya bayyana cewa wanna shiri na da matukar muhimmanci ga zaman lafiyar Najeriya.

Ya bayyana cewa mafi yawanci tubabbun ‘yan Boko haram din ba wai ra’ayi ne ya sakasu cikin lamarin ba, yawanci tursasa su aka yi ta hanyar garkuwa dasu da sauransu.

Yace idan gwamnati bata shiga lamarin tubabbun ‘yan Bòkò Hàràm din ba zasu iya zama cikin matsalar komawa ruwa sannan za’a iya rika waresu daga cikin al’umma.

Ya kuma jinjinawa Sojoji da sauran jami’an tsaro bisa kokarin da suke na wannan shiri. Sannan yri kiran a kara wayarwa da mutane kai game da shirin.

Shima a nashi bangaren Ali ya bayyana rashin jin dadin yanda mutane ke nuna kyama ga wadanda suka tuban.

Karanta Wannan  Masu ikirarin Jìhàdì sun kàshè manoma da masunta 40 a jihar Borno

Ya bayyana muhimmancin amfani da bangaren da bana karfi ba wajan yakar ‘yn Bindiga.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *