Thursday, February 5
Shadow

Allah Sarki: Kalli bidiyon Yanda wannan malamin ya sassauta lafazi akan Rasuwar Habu Dan Damisa, Yace Lamarinshi na gurin Allah a daina munana masa zato, bayan da a baya yayi wa’azi me kaushi sosai akan Dan Damusa amma yaran Dan Damusa suka gargadeshi

Wannan malamin ya fito ya sassauta lafazi akan wa’azi me kaushi da yayi a baya akan rasuwar dan daba, Habu Dan Damisa na Kaduna.

Malam a yanzu yace, a dauna munana zato akan dan Damisa inda yace lamarinsa na ga Allah, in yaso ya azabtar dashi in yaso ya yafe masa.

@ib_yusuf_muhd_sambo

DAN DAMISA… Duniya kenan, Wanda baizo ba ma tana jiransa. Ai da Babu mutuwa da shari’a, da wasu sunxci banza. Allah sa muyi karshe Mai kyau

♬ original sound – Ibrahim yusuf muh’d Sambo

Saidai da yawa sun ce malamin tsoro yaji kada yaran dan Damisa su illatashi ko kumama aikashi kiyama.

Karanta Wannan  Kalli Hotuna: Mata sama da 10 ne suka bayyana cewa suna son sojan ruwa AM. Yerima bayan dambarwarsa da Wike

A baya dai malam yayi Allah wadai da irin rayuwar dan Damisa inda ya kushe harkar daba duk da dai wa’azi ne yayi.

@ib_yusuf_muhd_sambo

HABU DAN DAMISA: Matashin Da Ya Yi Kàurin Sunà A Harkaŕ Daba A Yankin Tudun Wada Da Kewaye A Jihar Kaduna Ya Gamu Da Ajalinsa Saidai mutuwarsa ta raba hankulan jama’a, inda wasu ke jimami wasu kuma na mùrñà, duba da yadda ya aďdabi jama’à. Ko a wani bidiyo da aka nuno kusan yara ne zalla suka yi jana’izarsa.

♬ original sound – Ibrahim yusuf muh’d Sambo

Akwai wani matashi da ya fito yayi zagezage akan malamai, sannan ko a kasan Bidiyon malam an ga yanda ake mayar masa raddi masu zafi.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Abinda me wasan Barkwanci, Brother Shaggy yayi bayan da Senegal ta ci kofin AFCON a Morocco da ya dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *