Monday, March 17
Shadow

An kaiwa Tawagar Hadimar Gwamnan Kaduna hari

Hadimar gwamnan jihar Kaduna dake bashi shawara akan harkokin siyasa, Hon. Rachael Averik ta tsallake rijiya da baya a yunkurin kisheta da aka yi.

An kaiwa tawagar Hon. Rachael Averik harin kwantan baunane ranar Alhamis, 2 ga watan Janairu.

Harin ya farune a tsakanin kauyukan Tsauni Majidadi da Gani dake karamar hukumar Sanga ta jihar.

A ranar tana kan hanyar zuwa Gwantu ne abin ya faru.

A ranar taje gaisuwane sannan ta kaddamar da Asibitin da Alhaji Muhammad Umar Numbu ya gina a masarautar Arak.

Jami’an tsaron dake tare da ita sun budewa maharan wuta inda anan aka jikkata direbanta da Dansanda daya.

Jami’an tsaro a jihar sun fara bincike kan lamarin.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yanda matar shugaban kasar Botswana ta durkusa har kasa ta gaisheshi yayin da ake rantsar dashi

Gwamnatin jihar ta yi Allah wadai da harin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *