Saturday, May 10
Shadow

An kori malamin jami’ar ATBU Bauchi Dr. Usman Mohammed Aliyu saboda zargin aikawa dalibarsa matar aure sakonnin batsa sannan yace idan bata yadda yayi lalata da ita ba zai kayar da ita jarabawa

Jami’ar ATBU dake Bauchi ta sallami daya daga cikin malamanta me suna Dr. Usman Mohammed Aliyu bisa zargin neman yin lalata da dalibarsa wadda matar aurece.

Dalibar me suna Kamila Rufa’i Aliyu ta zargi malamin da cewa ya aika mata sakonnin batsa sannan ya nemi yayi lalata da ita.

Data kiya, sai ya ce zai kayar da ita jarabawa duk da cewa yasan ita matar aurece.

Saidai Dr. Usman ya shigar da kara kotu inda yake neman hakkinsa saboda a cewarsa, Kamila ta bata masa suna.

Mijin Kamila, Ja’afaru Buba ta hannun lauyansa ya shigar da karan makarantar inda ya bayar da dukkan hujjojin da yake dasu na cewa Dr. Usman ya nemi yin lalata da matarsa.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Bamu daga cikin wadanda Kudin mu zasu shiga hannun Bandit da sunan biyan kudin Fansa, idan har tsautsai yasa na shiga hannunsu to zan dauka Allah ya kaddaromin Shahadane ta wannan hanyar>>Sheikh Ibrahim Maqari

Bayan kammala bincike, Hukumar gudanarwar jami’ar ta ce ta samu Dr. Usman da laifi inda tace ta sallameshi daga aiki.

Sannan ya mika duk wani abu mallakin makarantar dake hannunsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *