Sunday, March 23
Shadow

APC ta goyi bayan Shugaba Tinubu kan saka dokar ta baci a jihar Rivers inda ta gargadi wani Gwamna tace yayi hankali saura shi

Sakataren jam’iyyar APC, Ajibola Basiru ya bayyana goyon bayan jam’iyyar su ga matakin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauka na dakatar da gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara.

A sanarwar da ya fitar daga kasar Saudiyya, Basiru yace lamuran tsaro sun runcabe a jihar Rivers amma gwamnan jihar ya ki tashi tsaye ya dauki mataki.

Yace suna fatan wannan mataki da shugaban kasa ya dauka ya kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Ya kara da kira ga shugaba Tinubu da ya dauki irin wannan mataki akan jihar Osun inda ya zargi gwamnan jihar da dakile ayyukan kananan hukumomi duk da umarnin kotu.

Karanta Wannan  Mutane 30 Sun Mutu An Kwantar Da Wasu Gommai a Asibiti Bayan Sun Sha Burkutu a India

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *