Thursday, May 22
Shadow

APC ta lashe duka ƙananan hukumomi 13 a zaɓen jihar Nasarawa

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulkin jihar Nasarawa a Najeriya ta lashe kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13 na jihar da aka yi.

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Nasarawa (NASIEC), Barr. Ayuba Usman, shi ne ya bayyana hakan a hedikwatar hukumar da ke Lafiya,babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa baya ga kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13, ƴantakarar jam’iyyar APC sun lashe kujerun kansila 140, yayin da jam’iyyar SDP ta lashe biyar, sai kuma Zenith Labour Party (ZLP) ta lashe biyu.

Kujerun kansilolin ZLP biyu suna cikin ƙaramar hukumar Doma, na SDP huɗu a Nasarawa-Eggon, da kuma ɗaya a ƙaramar hukumar Keffi.

Karanta Wannan  Maraba Da Watan Mauludin Shugaba Sallallahu Alaihi Wasallam! Ya Allàh Ka Hore Mana Watan Máụludi Da Abun da Ya Ƙunsa, Ka Buɗe Mana Manyan Taskoki Na Arziƙi Domin Mu Yi Hidima Cikin Wànnan Watan Mai Albarka, Cewar Ɗan Ƙasar Chana, Masanin Hausa, Malam Murtala Zhang

Ya ce jam’iyyun siyasa 14 ne suka fafata a zaben, yana mai cewa amfani da fasaha ya ƙara sanya zaɓen ya kasance mai inganci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *