Friday, December 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon yanda Gobara ta tashi a wajen sayar da Gas a Rijiyar Zaki Kano, Ji yanda Tukwanen Gas suka rika fashewa suna kara kamar Bàm

Kalli Bidiyon yanda Gobara ta tashi a wajen sayar da Gas a Rijiyar Zaki Kano, Ji yanda Tukwanen Gas suka rika fashewa suna kara kamar Bàm

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kano na cewa an samu fashewar tukunyar gas a wani wajan sayar da gas din dake Dorawar 'yan Kifi, Rijiyar Zaki. A bayanan da hutudole ya samu shine ba'a samu asarar rayuka ko jikkata ba saidai asarar Dukiya. A bidiyon da suka rika yawo a kafafen sada zumunta, an ga da jin yanda tukwanen gas din duka rika fashewa kamar bam na tashi. https://www.tiktok.com/@kingkadoo1/video/7495415482929974583?_t=ZM-8vhcbEDH8TN&_r=1 https://www.tiktok.com/@kingkadoo1/video/7495418146510179639?_t=ZM-8vhcgdjSPDT&_r=1 https://www.tiktok.com/@kingkadoo1/video/7495422464655101189?_t=ZM-8vhcl2xDLao&_r=1 https://www.tiktok.com/@a.k.a.i.s.u/video/7495433889079463174?_t=ZM-8vhcsqiCr3O&_r=1 Saidai daga baya 'yan kwana-kwana sun kai wajan sun kashe gobara...
Kiran mutane su tashi tsaye su kare kansu bashine mafita ba ga matsalar tsaro>>Bulama Bukarti ya mayarwa da T.Y Danjuma Martani bayan da yace mutane su tashi tsaye su kare kansu Gwamnati ba zata iya ba ita kadai

Kiran mutane su tashi tsaye su kare kansu bashine mafita ba ga matsalar tsaro>>Bulama Bukarti ya mayarwa da T.Y Danjuma Martani bayan da yace mutane su tashi tsaye su kare kansu Gwamnati ba zata iya ba ita kadai

Duk Labarai
Babban me sharhi akan Al'amuran tsaro, Bulama Bukarti ya mayarwa da Tsohon Ministan tsaro, T.Y Danjuma martani kan kiran da yayi mutane su tashi tsaye su kare kansu game da matsalar tsaro. T.Y Danjuma yace gwamnati ba zata iya ba ita kadai inda yace kamata yayi mutane su tashi su kare kansu. Saidai a hirar da aka yi dashi a Channels TV, Bulama Bukarti ya bayyana cewa wannan ba mafita bace. Yace idan aka yi hakan, makamai zasu karu a hannun farar hula wanda hakan zai kawo ci gaba da kisan mutane ba tare da hukunci ba.
2027: Nan da watanni 6 yankin Arewacin Najeriya zai bayyana matsayar sa kan zaben shugaban kasa – Hakeem Baba-Ahmed

2027: Nan da watanni 6 yankin Arewacin Najeriya zai bayyana matsayar sa kan zaben shugaban kasa – Hakeem Baba-Ahmed

Duk Labarai
2027: Nan da watanni 6 yankin Arewacin Najeriya zai bayyana matsayar sa kan zaben shugaban kasa - Hakeem Baba-Ahmed. Hakeem Baba-Ahmed, tsohon mai bai wa Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima shawara kan harkokin siyasa, ya yi gargadin cewa Arewacin Najeriya na iya daukar matsaya mai tsauri dangane da makomar siyasar yankin idan aka ci gaba da watsi da koke-koken yankin. A cikin wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, Baba-Ahmed ya bukaci ‘yan Arewa da su ci gaba da kasancewa tsintsiya madaurinki daya tare da lura da "makaryata" da ke aiki don raunana yankin. “Arewacin Najeriya za ta tsaya ta kare kanta, wallahi,” in ji shi. “Ya kamata Arewa ta yi hattara sosai, ta guji ‘yan siyasa na cin amana da kuma duk wani abu da zai kawo rabuwar kai.” Ya jaddada bukatar h...
Da Duminsa: Cikin darennan Bàm ya fashe a gidan yarin Maiduguri jihar Borno

Da Duminsa: Cikin darennan Bàm ya fashe a gidan yarin Maiduguri jihar Borno

Duk Labarai
Rahotanni daga Maiduguri na cewa wani abin fashewa me kama da bam ya fashe a gidan yarin dake garin da daren Ranar Lahadi. Lamarin ya farune da misalin karfe 9 na darennan inda hakan yayi sanadiyyar tashin wuta a dakin da ake tsare da Charles Okah. Wasu shaidu sun ce an cilla wani abu me kama da bam a dakin da ake tsare da Charles Okah din inda aka ga hayaki na tashi. Wannan lamari ya biyo bayan budaddiyar wasikar da Charles Okah ya aikewa ministan harkokin cikin gida, Olubunmi-Ojo ne inda yake korafi kan yawaitar cin hanci a gidajen yarin Maidugurin. Rahoton na Sahara reporters yace Okah ya rika tari inda aka ji yana fadin an cilla masa bom a dakinsa. Saidai babu wanda ya kai masa dauki dan kuwa a cewar rahoton ma'aikatan gidan yarin dake aikin dare basa nan. Hakanan wan...
Taliya Ba Za Ta Yi Tasiri Ba A Zaɓen 2027 Saboda Kan Mage Ya Waye, Cewar Sanata Babba Kaita

Taliya Ba Za Ta Yi Tasiri Ba A Zaɓen 2027 Saboda Kan Mage Ya Waye, Cewar Sanata Babba Kaita

Duk Labarai
Taliya Ba Za Ta Yi Tasiri Ba A Zaɓen 2027 Saboda Kan Mage Ya Waye, Cewar Sanata Babba Kaita. Wayewa a siyasa ita ce damawa da kowa ba tare da la’akari da ƙabila ko addini ko yankin da mutum ya fito ba, don haka ya zama wajibi a dama da dukannin bangarorin ƙasar nan muddin ana yin siyasa ne don cigaban al’umma. Yin wani abu akasin haka kuskure ne babba a siyasance, domin mutane ba su da mantuwa. Komai daren daɗewa za su rama abin da aka yi musu idan lokacin yin ramuwar ya zo. Duk da cewa mutane na cikin yunwa da fatara, a wannan karon Taliyarka ba za ta yi ma amfanin komai ba saboda kan mage ya waye! Daga Jamilu Dabawa
Kalli Bidiyon hudubar da uba yawa diyarsa bayan daurin aure da ta dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon hudubar da uba yawa diyarsa bayan daurin aure da ta dauki hankula sosai

Duk Labarai
Wani mahaifi bafulatani ya dauki hankulan mutane sosai musamman a kafafen sadarwa bayan da aka ga irin hudubar da yawa diyarsa da aka daurawa aure. Bidiyon hudubar ya watsu sosai a kafafen sadarwa inda ake ya sanya masa Albarka. Ya gargadi diyarsa kada ta sake ta saurari kowa idan ba mijinta ba. https://www.tiktok.com/@fulani_tutor/video/7232318925684460805?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7232318925684460805&source=h5_m&timestamp=1745185435&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7483198445273974549&am...
Atiku ya nemi Peter Obi ya zama mataimakinsa a 2027 dan su kwace mulki a hannun Tinubu, inda shi kuma yayi Alkawarin yin mulki sau daya ya sauka ya barwa Peter Obin

Atiku ya nemi Peter Obi ya zama mataimakinsa a 2027 dan su kwace mulki a hannun Tinubu, inda shi kuma yayi Alkawarin yin mulki sau daya ya sauka ya barwa Peter Obin

Duk Labarai
Rahotanni daga bangaren Atiku na cewa jiga-jigai sun nemi hada kai da Peter Obi ganin yana da mabiya sosai musamman a kudancin Najeriya. Rahoton yace an nemi goyon bayan Peter Obi dan ya zama mataimakinsa a shekarar 2027 dan su kwace mulki daga hannun shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Rahoton yace bangaren Atiku sun yi Alkawurin yin mulki sau daya inda a shekarar 2031, za'a barwa Peter Obi shi kuma yayi takarar shugaban kasa. Saidai bangaren Peter Obi sun ki amincewa inda suka ce ai kudu bata kammala wa'adinta na zango biyu ba kamar yanda Buhari yayi. Dan haka suka ce idan ba Peter Obi bane zai zama ahugaban kasa ba, to basu yadda ba. Saidai ana ganin har yanzu wannan tattaunawa bata kare ba inda ake tsammanin zata iya cimma gaci.
Kalli Bidiyo: Tinubu dan Kanone>>Inji Ganduje

Kalli Bidiyo: Tinubu dan Kanone>>Inji Ganduje

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar APC, Umar Abdullahi Ganduje ya bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dan Kanone kuma sunansa Ashiru. Ya bayyana cewa da aka kaishi Legas ne sai yarbawa suka mayar dashi Asiwaju. Yace kuma dayan sunansa shine Bala inda Yarbawa nan ma suka mayar dashi Bola. Kalli Bidiyon anan https://www.youtube.com/watch?v=Olv-J_MF5gQ?si=tgPP_rA4LORA_o-w Gandune ya bayyana hakane a wani bidiyo da ya yadu sosai a kafafen sadarwa.
Manyan Limaman Kiristoci sun yi ruwan Allah wadai ga gwamnatin Tinubu inda suka ce Ya magance matsalar Talauci data tsaro

Manyan Limaman Kiristoci sun yi ruwan Allah wadai ga gwamnatin Tinubu inda suka ce Ya magance matsalar Talauci data tsaro

Duk Labarai
Manyan malaman kiristoci sun yi ruwan Allah wadai ga gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda suka bukaci da ya kawo hanyar kawar da matsalar tsaro data talauci da matsin tattalin arziki. Sun bayyana hakanne a sakonnin bukukuwan Easter daban-daban da suka fitar. Misali babban fasto, Bishop Matthew Hassan Kukah ya misalta halin da Najeriya ke ciki da lokacin da aka gicciye Yesu inda yace Tinubu ya sauko da mutanen Najeriya daga gicciyewar shedan. Bishop Kuka yayi kira ga gwamnatin data dauki matakan gaggawa na kawo karshen matsalolin tsaro da yunwa da sauransu. Yace mafi yawancin 'yan Najeriya sun yanke tsammanin samun canji amma su a matsayinsu na kirista basu yanke tsammani ba. Yace duk da ba Tinubu bane ya saka 'yan Najeriya a cikin wannan hali ba amma yana Kiran ...
Fararoma yayi kiran a yi Sulhu a Gaza

Fararoma yayi kiran a yi Sulhu a Gaza

Duk Labarai
Babban Limamin Kirista, Fafaroma Francis ya nemi a yi sulhu a yakin da ake tsakanin kungiyar Hamas da Israela. Yayi wannan kirane a yayin da ake bukukuwan Easter. Yawan wanda aka kashe a Falasdin ya haura mutane dubu 50 ciki hadda mata da kananan yara. Fafaroma ya kuma bayyana a karin farko tun bayan da yayi doguwar rashin lafiya a bainar jama'a. Hakanan Mataimakin shugaban kasar Amurka, J.D Vance ya halarci fadar Fafaroman yayin da ake bukukuwan Easter.