Saturday, February 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Hisba ta kama matasan da ba sa yin azumi da masu askin banza a Kano

Hisba ta kama matasan da ba sa yin azumi da masu askin banza a Kano

Duk Labarai
Jami’an Hukumar Hisba a jihar Kano sun kama wasu matasa gandaye da ake zargi da kin yin azumi a ranar farko ta watan Ramadan. Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahideen Abubakar ne ya tabbatar da kamen ga manema labarai a jihar. Ya kara da cewa an kama matasan ne yayin sintiri da jami’an hukumar ke yi a sassa daban-daban na birnin Kano. Haka kuma, hukumar ta cafke kimanin mutane 60 da ke da askin banza, wanda ya sabawa dokokin shari’a da al’adun gari. Bugu da kari, Hisba ta kama wasu direbobin baburan adaidaita sahu (keke napep) da ake zargi da cakuda maza da mata a baburansu, lamarin da hukumar tace ba za ta lamunta da shi ba. Hukumar ta Hisba ta bayyana cewa za ta ci gaba da gudanar da sintiri don tabbatar da bin dokokin shari’a a cikin watan Ramadan.
Kalli bidiyon yanda wani yayi kashin kullin Kwàyòyì 120 da ya hadiya yana shirin fita dasu kasashen waje

Kalli bidiyon yanda wani yayi kashin kullin Kwàyòyì 120 da ya hadiya yana shirin fita dasu kasashen waje

Duk Labarai
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, NDLEA ta kama wani mutum da me suna Mbala Dajou Abuba a filin sauka da tashin jiragen sama na Mallam Aminu Kano dake Kano yana shirin fita da kwayoyi zuwa kasashen waje. An kama mutumin da ya hadiyi kullun Hodar Iblis da yawa yana shirin fita da ita zuwa Istanbul babban birnin kasar Turkiyya. Mutumin dan asalin Zaire ne ta kasar Angola kuma an kamashine ranar Talata, February 25, 2025 inda yake shirin hawa jirgin sama zuwa kasar Egypt wanda daga can zai wuce zuwa kasar Turkiyya. Kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya bayyana cewa mutumin yace yana aikin kai sakonnine a kasarsa ta Angola kamin ya fada harkar safarar kwaya. alli Bidiyon anan
Ji yanda ‘yan Bìndìgà suka yi shiga irin ta EFCC suka je wani Otal suka kwashe mutanen ciki a jihar Naija

Ji yanda ‘yan Bìndìgà suka yi shiga irin ta EFCC suka je wani Otal suka kwashe mutanen ciki a jihar Naija

Duk Labarai
' Yan Bindiga masu garkuwa da mutane sun yi basaja inda suka yi shiga irin ta jami'an hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC suka shiga otal din White Hill Hotel dake Chanchaga a jihar Naija suka yi garkuwa da mutane. Lamarinnya farune ranar Talata February 27, 2025 da misalin karfe 4:58 na dare. 'Yan Bindigar sun lalata kyamarorin CCTV dake ital din kamin suka shiga daki-daki suka dauki mutane akalla 10 suka yi awon gaba dasu Hukumar 'yansandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace suna kan kokarin gano wadanda suka yi wannan aika-aika da kuma kubutar da wadanda aka sace.
Kalli Hotuna: Gagga-gaggan ƴan Bìndìgà 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba

Kalli Hotuna: Gagga-gaggan ƴan Bìndìgà 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba

Duk Labarai
Gagga-gaggan ƴan bindiga 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba Sun kuma mika bindigar AK49 har guda biyu don tabbatar da tubansu An kai ƙarshen zaman tattaunawa tareda da tubabbun yan dindiga a karamar hukumar Jibia ta jahar Katsina. A ranar Juma'a 28/2/2025, ne aka kai ƙarshen zaman tattaunawa da yan dindigar da suka shirya karɓar zaman lafiya a karamar hukumar Jibia a jihar Katsina. Anyi zaman a karkashin jagorancin Chairman na karamar hukumar Jibia da Jibiya Peoples Froum da (NCSOSACK) da rundunar sojin Nigeriya ta jihar Katsina, daga cikin tubabbun yan dindigar da a kayi zaman tattaunawar dasu akwai.1- Audu Lanƙai2- Kantoma3- Ori4- Tukur Dan Najeriya5- Bammi. A yayin zaman an tattauna batutuwa da da dama da kuma shimf...
Yan bìndigà sun sace dalibai 4 maza na Jami’ar FUDMA a jihar Katsina

Yan bìndigà sun sace dalibai 4 maza na Jami’ar FUDMA a jihar Katsina

Duk Labarai
Wasu 'yan bindi-gà masu garkuwa da mutane sun kutsa gidan ƙwanan daliban Jami'ar gwamnatin Tarayya ta FUDMA da ke garin Dutsin-ma, a jihar Katsina, inda suka yi awon gaba da dalibai 4 maza zuwa daji don neman fudin fansa. Lamarin ya faru a daren ranar Lahadi 2 ga watan March 2025 a rukunin gidajen dake unguwar bayan gidan Radio kusa da mazaunin jami'ar na wucin gadi. Ya zuwa yanzu dai ba a san inda aka nufa da daliban ba. Kalli bidiyon anan MUN DAUKO RUBUTUN DAGA SHAFIN KATSINA REPORTS
Ni zan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027>>Inji Sowore bayan da ya shiga aka yi gudun fanfalaki dashi

Ni zan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027>>Inji Sowore bayan da ya shiga aka yi gudun fanfalaki dashi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na Jam'iyyar AAC a zaben shakerar 2019 da 2023, Omoyele Sowore kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters ya shiga gudun yada kanin wani da aka yi a Abuja. Ya bayyana cewa shine zai kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sauran 'yan takarar shugaban kasa a zaben 2027. Yace ya kamata Gwammati ta baiwa bangaren wasannin motsa jiki muhimmanci inda yace suma zasu iya kawo kudaden shiga kamar yanda fetur ke kawowa kasarnan.
Magidanci ya kkàshe Matarsa saboda rikicin abincin shan ruwa a jiya bayan an kai Azumin farko a jihar Bauchi

Magidanci ya kkàshe Matarsa saboda rikicin abincin shan ruwa a jiya bayan an kai Azumin farko a jihar Bauchi

Duk Labarai
DA DUMI-DUMI: Miji Ya Kashe Matarsa a Bauchi Saboda Abincin Buda Baki. Rundunar ‘Yan Sanda Ta Fara Bincike Kan Kisan Wasila Abdullahi Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta fara bincike kan wani mummunan lamari da ya faru a daren Asabar, 1 ga Maris, 2025, inda wani attajiri mai suna Alhaji Nuru Isah, mai shekaru 50, ya buge matarsa, Wasila Abdullahi, mai shekaru 24, har lahira. Bayanan da aka tattara sun nuna cewa rikici ya barke tsakanin ma’auratan ne a gidansu da ke kusa da makarantar GG Bauchi a unguwar Fadamam Mada, kan yadda za a raba kayan abinci da ‘ya’yan itatuwa don buda baki a watan Ramadan. Wani makwabci ya ce takaddamar ta rikide zuwa fada, inda Alhaji Nuru Isah ya dauki sanda ya bugi matarsa, wanda hakan ya sa ta fadi sumammiya. Bayan haka, an garzaya da ita asibitin...
Dalilin da yasa na koma Jam’iyyar APC>>Shehu Sani

Dalilin da yasa na koma Jam’iyyar APC>>Shehu Sani

Duk Labarai
Sanata Shehu Sani ya bayyana dalilin da yasa ya koma Jam'iyyar APC. Sanata Sani ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV. Yace Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ne ya jawoshi ya koma Jam'iyyar ta APC. Yace dama can yana daga cikin wadanda suka kafa jami'iyyar a Kaduna har aka ci zabe. Yace sun samu rashin jituwa da Gwamna El-Rufai ne a wancan lokacin shiyasa suka bar Jam'iyyar kuma yanzu Gwamna Uba sani ya dawo dasu.
Ashe ba yau aka fara ba: Yanda wata mata ta taba Fallawa Sanata Godswill Akpabio mari bisa zargin cewa ya bata makudan kudi dan ta amince yayi lalata da ita

Ashe ba yau aka fara ba: Yanda wata mata ta taba Fallawa Sanata Godswill Akpabio mari bisa zargin cewa ya bata makudan kudi dan ta amince yayi lalata da ita

Duk Labarai
A yayin da dambarwar sanata Natasha Akpoti da Godswill Akpabio ke ci gaba da bayyana inda take zarginsa da cewa ya nemi yin lalata da ita. An koma baya a tarihi a lokacin Sanata Godswill Akpabio yana ministan Ma'aikatar harkokin Niger Delta, Tsohuwar shugabar riko ta hukumar raya yankin Niger Delta watau NDDC, Joy Nunieh ta zargeshi da cewa ya nemi yin lalata da ita. A wancan lokacin har fallaasa mari ta yi inda tace dalili shine ya bata kudi wai ta yadda yayi lalata da ita. Matar dai itama ta bayyana wannan zargi ne a gidan talabijin na Arise TV inda tace yana tunanin zai iya canja mata tunani da kudi? Tace itace mace ta farko data taba falla masa mari amma yaki gayawa mutane kuma tana zarginsa da neman yin lalata da ita. Saidai a wancan lokacin Akpabio yace bata da lafiya ...
An kama Fasto da yin mu’ujizar karya inda yace ya mayar da wata mata me kudi amma sai bayan kwanaki aka ganta tana sayar da Lemun Kwalba

An kama Fasto da yin mu’ujizar karya inda yace ya mayar da wata mata me kudi amma sai bayan kwanaki aka ganta tana sayar da Lemun Kwalba

Duk Labarai
Wani fasto me suna Ebuka Obi ya shiga idon Duniya bayan da aka kamashi yana yiwa mabiyansa karya ta hanyar mu'ujizar karya. Faston dai ya kai wata mata cocinsa me suna Zion Prayer Movement Outreach inda ta yi ikirarin cewa da tana da 300,000 amma data hadu da faston kudinta sun yi albarka har ta sayi gidan Miliyan 500 a Lekki jihar Legas. Saidai kwanaki bayan yin wannan ikirari, An ga matar tana sayar da lemun Kwalba. Matar dai har wani gida ta je ta nuna wanda tace nata ne amma daga baya me gidan sai da ya kamata akan ikirarin da ta yi na gidansa. A baya dai, Faston ya taba yin ikirarin warkar da marigayi dan fim din Kudu, John Okafor wanda aka fi sani da Mr. Ibu daga cutar dake damunsa amma kuma sai gashi daga baya dan fim din ya mutu. Faston dai na ikirarin cewa shi annab...