Thursday, March 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kaso 90 cikin 100 na Kiristocin da ake ķķàshèwà a Duniya a Najeriya ake ķķàshèsu, Najeriya ta kasa baiwa Kiristoci kariya dan haka zamu Kakaba mata Takunkumi>>Inji Kasar Amurka

Kaso 90 cikin 100 na Kiristocin da ake ķķàshèwà a Duniya a Najeriya ake ķķàshèsu, Najeriya ta kasa baiwa Kiristoci kariya dan haka zamu Kakaba mata Takunkumi>>Inji Kasar Amurka

Duk Labarai
Majalisar kasar Amurka ta baiwa shugaban kasar, Donald Trump shawarar ya kakabawa Najeriya takunkumi saboda yawan kashe kiristoci da ake yi a kasar. Majalisar ta cimma wannan matsayane bayan samun bayanai daga wani bincike da aka gudanar da yake nuna cewa kaso 90 na kiristocin da ake kashewa a Duniya a Najeriya ne hakan ke faruwa. Majalisar ta kasar Amurka ta zargi Najeriya da kasa daukar matakan da suka kamata dan baiwa Kiristocin kariya daga hare-haren ta'addanci dake yin sanadiyyar mutuwarsu. Saidai a martanin Gwamnatin Najeriya tace wannan magana ba gaskiya bace. Sanarwar da ma'aikatar harkokin kasashen waje ta Najeriya ta fitar ta hannun kakakinta, Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya bayyana cewa, tabbas akwai matsalar tsaro a Najeriya. Amma ba wani addini daya aka ware shi k...
Hukumar babban birnin tarayya, Abuja ta kwacewa PDP filinta da babban Ofishinta na kasa dake Abuje ke gine

Hukumar babban birnin tarayya, Abuja ta kwacewa PDP filinta da babban Ofishinta na kasa dake Abuje ke gine

Duk Labarai
Hukumar kula da babban birnin Tarayya, Abuja, FCTA ta kwace filin hedikwatar jam'iyyar PDP dake Abuja. A takardar kwace filin da hutudole ya karanta, hukumar FCTA tace PDP taki biyan harajin da ya kamata ta biya na kan filin kusan tsawon shekaru 20 da suka gabata kenan. Kuma tun shekarar 2023 ake ta tunatar da PDP game da biyan harajin amma ta yi kunnen uwar shegu. Dan hakane yanzu an kwace filin ya zama mallakin hukumar FCTA din dake Abuja.
Banda mu a cikin wadanda suka saci man fetur daga tankar mai data fadi, Bidiyon karyane ake yadawa>>Inji Hukumar ‘yansandan Najeriya

Banda mu a cikin wadanda suka saci man fetur daga tankar mai data fadi, Bidiyon karyane ake yadawa>>Inji Hukumar ‘yansandan Najeriya

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta musanta cewa an ga jami'anta suna kwasar man fetur bayan da wata tankar mai ta fadi. Bidiyo ya watsu sosai inda aka ga wasu da kayan 'yansandan suma sun shiga sahu masu satarman daga tankar. Saidai a sanarwar da kakakin hukumar 'yansandan ta kasa, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, yace ba 'yansandan Najeriya ne ba a bidiyon, 'yansandan makwabtan Najeriya ne. Ya kara da cewa, an saki Bidiyonne kawai dan a batawa hukumar 'yansandan Najeriya suna. Yace jami'an tsaron dake bidiyon, faransanci suke ba Turanci ba yace dan haka ba 'yansandan Najeriya bane. Yace hukumar 'yansanda tana nan kan gudanar da aikinta bisa doka da kwarewa. Ya gargadi mutane su daina yada labarin da bai inganta ba.
Girman kai da haushine cike da zuciyar El-Rufai saboda bai samu Minista ba shiyasa ya koma SDP>>Inji APC

Girman kai da haushine cike da zuciyar El-Rufai saboda bai samu Minista ba shiyasa ya koma SDP>>Inji APC

Duk Labarai
jam'iyyar APC ta caccaki tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ta bayyanashi a matsayin wanda ke ci ke da girman kai da haushi saboda bai samu mukamin minista ba. Sakataren jam'iyyar, Felix Morka ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace El-Rufai ya kamata idan zai soki gwamnatin Tinubu yayi suka ta adalci. Felix yayi watsi da ikirarin El-Rufai na cewa jam'iyyar APC ta kauce daga kan turbar da aka kafata inda yace gwamnatin Tinubu ta samu ci gaba sosai da suka hada da cire tallafin man fetur da daidaita canjin kudi da sauransu.
Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Duk Labarai
Har yanzu dai Sanata Natasha Akpoti bata saurara ba da yiwa kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio tonon silili. A sabuwar hirar da ta yi da BBC Pidgin, Natasha tace majalisarsu kamar kungiyar tsafi take. Tace kowane sanata na tsoron ya bayyana ra'ayin da ya sha banban da na kakakin majalisar saboda tsoron kada a saka masa ido. Tace amma zargin da takewa Sanata Godswill Akpabio da gaskene, ta sake maimaita cewa akwai sanda suka je gidansa ya kama hannunta a gaban mijinta ya ja ya suna tafiya, tace ya rika murza mata hannu, tace kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi. Tace hakanan akwai sanda ta manta ta tafi aiki da sauri bata dauki zoben alkawarinta na aure ba, tace Sanata Godswill Akpabio na ganinta sai yake ce mata yaya Natasha, naga baki saka zoben aurenk...
Dan Fim Din Kudu ya bayar da labarin yanda abokan aikinsa mata 3 suka masa fyàdè a yayin da suke wani otal daukar fim

Dan Fim Din Kudu ya bayar da labarin yanda abokan aikinsa mata 3 suka masa fyàdè a yayin da suke wani otal daukar fim

Duk Labarai
Dan fim din kudu, Lanre Adediwura ya bayyana yanda wasu mata 3 abokan aikinsa suka masa fyade a yayin da yaje aikin daukar wani fim. Yace da farko dai ya je wajan daukar fim dinne inda daga baya wata abokiyar aikinshi ta sameshi ta bayyana masa cewa, tana sonsa. Yace a nan ya sanar da ita yana da aure amma tace ta ji ta gani. Ya kara da cewa anan suka zauna suna buga karta ko wasan kati, da suka gama dare yayi, ya manta katin a hannunta. Yace ta je dakin otal dinsa dan ta kai masa katin, inda anan ne ya ganta da abokanta biyu sun je su masa fyade. Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda lamarin ya jawo cece-kuce.
A kudancin Kaduna, Gwamnatin mu ta APC bata tabuka abin Arziki ba>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

A kudancin Kaduna, Gwamnatin mu ta APC bata tabuka abin Arziki ba>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, Gwamnatinsu ta APC bata tabuka abin a zo a gani ba a kudancin jihar kaduna. Ya bayyana hakane a matsayin suka ga gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. El-Rufai ya shafe shekaru 8 yana a matsayin gwamnan Kaduna saidai a kwanannan ya bar jam'iyyar APC zuwa PDP. A ci gaba da bayaninsa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, Amma gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta canja akalar yankin inda ta kawo mai ci gaba. Ya bayar da misali na ci gaban da gwamnatin Tinubu ta kai yankin kudancin jihar Kaduna inda yace kwanannan Shugaba Tinubun ya sakawa kudirin dokar samar da jami'ar kimiyya da fasaha ta Federal University of Applied Sciences hannu wadda za'a bude a karamar hukumar Kachia.
El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani na Kaduna da sace kudaden kananan hukumomi ya je kasashen Ingila da Afrika ta kudu ya sayi gidaje

El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani na Kaduna da sace kudaden kananan hukumomi ya je kasashen Ingila da Afrika ta kudu ya sayi gidaje

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya zargi Gwamnan jihar me ci, Malam Uba Sani da yin amfani da kudaden kananan hukumomi ya sayi gidaje a kasashen Seychelles, South Africa, da the United Kingdom.  EL-RUFAI wanda bai dade da barin jam'iyyar APC zuwa SDP ba ya bayyana hakane a yayin hirar da aka yi dashi a gidan rediyon Najeriya dake Kaduna ranar Talata. Yace gwamna Uba Sani na karkatar da kudaden kananan hukumomi inda yake canjasu zuwa dala bisa shirin sayen gidaje. Yace amma shi a zamanin mulkinsa ba abinda yayi kenan ba. Yace a zamaninsa suna baiwa kananan hukumomi kudadensu, yace shuwagabannin kananan hukumomi na APC da PDP duk suna nan da rai kuma zasu iya bayar da shaida akan hakan. Yace amma hukumomin gwamnatin tarayya sun ki cewa uffan kan abinda...
Tanko Yakasai yayi kiran Arewa ta ci gaba da goyon bayan Shugaba Tinubu saboda kokarinsa na tada komadar tattalin arziki na samar da sakamako me kyau

Tanko Yakasai yayi kiran Arewa ta ci gaba da goyon bayan Shugaba Tinubu saboda kokarinsa na tada komadar tattalin arziki na samar da sakamako me kyau

Duk Labarai
Dattijon Arewa, Alhaji Tanko Yakasai ya yabawa Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda kokarin tayar da komadar tattalin arzikin da take. A bayanin da ya yiwa 'yan Jarida ranar Lahadi a Kano, Tanko Yakasai ya bayyana cewa, 'yan Najeriya sun fara samun sauki daga matsin tattalin arzikin da suke fuskanta. Yace farashin kayan masarufi da na man fetur na ci gaba da sauka. Yakasai yayi kira ga 'Yan Arewa dama Najeriya baki daya dasu ci gaba da baiwa gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu goyon baya. Ya bayyana cewa, Gwamnatin Tinubu na kokarin samar da ci gaban kasa kuma Arewa ba'a barta a baya ba a wannan kokari.
Me magana da yawun shugaban kasa ya nemi a zartar da hukuncin ķķìsà kan matashiya ‘yar bautar kasa data soki Gwammatin Tinubu

Me magana da yawun shugaban kasa ya nemi a zartar da hukuncin ķķìsà kan matashiya ‘yar bautar kasa data soki Gwammatin Tinubu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, me taimakawa shugaban kasa kan yada labarai, Temitope Ajayi ya nemi a zartar da hukuncin kisa kan matashiya Ushie Uguamaye saboda sukar da tawa shugaba Bola Ahmad Tinubu. Kafar peoplesgazette ce ta wallafa cewa Temitope Ajayi ya nemi a yankewa Ushie hukuncin kisa saboda yace a zartar mata hukunci mafi tsanani da hukumar bautar kasa ta NYSC ta tanadar. Saidai a bayaninsa, Ajayi, ya bayyana cewa, shi ba haka yake nufi ba, an canja masa manufar bayaninsa ne dan cimma wani buri. Yace abinda yake nufi da zartarwa da Ushie hukunci mafi tsanani a dokar NYSC shine a koreta daga aikin bautar kasar, yace shi a iya saninsa wannan ne hukunci mafi tsanani a dokar NYSC ba hukuncin kisa ba. Lamarin Ushie ya dauki hankula sosai inda ciki hadda Atiku Abubakar, da Pet...