Wednesday, July 1
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Giya ce dalili na 3 na kamuwa da cutar daji(cancer)

Giya ce dalili na 3 na kamuwa da cutar daji(cancer)

Duk Labarai
Babban masanin kiwon lafiya na kasar Amurka ya bayar da shawarar cewa kamata yayi ace duk giyar a ake sayarwa a kasar a saka mata gargadi na cewa shanta zai iya kai mutum ga kamuwa da cutar daji(Cancer), kamar dai yanda gargadin yake a jikin kwalayen taba. Vivek Murthy’s ya bayyana cewa shan giya na cike da hadarin kamuwa da cutar Daji(Cancer) akalla kala bakwai ciki hadda Cancer nono data hanji da sauransu. Yace bayan yawan kiba da taba sigari, Shan giya shine abu na 3 da za'a iya hakura dashi dan kaucewa kamuwa da cutar daji. Rahoton na jaridar New York Post yace shan giya na sanadin kamuwar mutane akalla dubu dari da cutar Cancer wanda kuma take sanadiyyar kisan mutane akalla dubu ashirin duk shekara. Wannan adadi yafi mace-macen da ake samu sanadiyyar hadarin mota. Masu ...
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kaiwa tsohon kwamishinansa, Bashir Sa’idu dake daure a gidan yari kan zargin satar sama da Naira Biliyan 3 ziyara

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kaiwa tsohon kwamishinansa, Bashir Sa’idu dake daure a gidan yari kan zargin satar sama da Naira Biliyan 3 ziyara

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kaiwa tsohon Kwamishinansa,Bashir Sa'idu ziyara a gidan yari. An kama Tsohon kwamishinan ne bisa zargin satar kudi da cin amana. Wasu daga cikin laifukan da ake zarginsa dasu sun hada da sayar da daloli daga asusun ajiyar kudi na jihar akan farashin Naira 410 maimakon farashin 498. Wanda hakan ya kawowa Gwamnatin asarar Naira Biliyan 3.96. Sannan kuma akwai maganar sayar da rukunin gidajen Marafa wanda shima ana neman Naira Miliyan 244 daga hannun tsohon kwamishinan. Wasu dai sun yi zargin bita da kullin siyasa a zarge-zargen da akewa tsohon kwamishinan amma hukumomi sun yi Alkawarin yin Aldaci a binciken da akewa tsohon Kwamishinan. Bayan ziyarar tasa, El-Rufai yaki yace uffan kan abinda ya faru inda ya shiga mota ya...
Bamu hada kai da kowace Jam’iyya ba kan maganar 2027>>Peter Obi

Bamu hada kai da kowace Jam’iyya ba kan maganar 2027>>Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na Jam'iyyar Labour Party a shekarar 2023, Peter Obi ya bayyana cewa babu wata yarjejeniyar hadaka da aka cimma tsakaninsa da wata jam'iyyar Adawa. Peter Obi ya bayyana hakanne a Abuja yayin ganawa da manema labarai. Saidai bai karyata cewa akwai tattaunawa da ake tsakaninsa da jam'iyyun Adawa ba amma yace ba'a cimma yarjejeniya ba. Peter Obi ya bayyana cewa akwai bukatar samun hadin kai tsakanin 'yan Najeriya ba tare da la'akari da banbancin Jam'iyya ba inda yace ta hakane kadai za'a samu nasarar kwace mulki daga hannun APC dake mulkin kama karya a Najeriya. Ya bayyana damuwa kan cewa 'yan Najeriya da yawa bmna bakuntar Lahira basu shirya ba saboda matsalolin tsaro da gwamnati ta kasa shawo kansu
Gwamnatin tarayya zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da matatar man fetur ta Dangote

Gwamnatin tarayya zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da matatar man fetur ta Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya na shirin rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da kamfanin matatar man Dangote. Hakan na zuwane bayan da matatun man fetur na Gwamnati, na Fatakwal dana Warri suna dawo suka ci gaba da aiki. Rahoton jaridar Punchng ya ruwaito cewa dan samarwa wadannan matatun man fetur na gwamnati isashshen danyen man fetur din, Gwamnatin zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa matatar man fetur ta Dangote. Hakan, a cewar masana tattalin Arziki, zai sa a samu gasa sosai a kasuwar man fetur din wanda hakan zai yi sanadiyyarf faduwar farashin man fetue din.
A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura

A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura

Duk Labarai
A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Shehin Malamin ya bada baburan ne bayan alkawarin da ya yi musu a yayin da suke taron tsoffin dalibai.
Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina

Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina

Duk Labarai
Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar 'Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina. A Karkashin Jagorancin Kwamishinan Yansanda, Aliyu Abubakar Musa A Cikin Shekarar Da Ta Gabata, Wanda Jami'in Hulda Da Jama'a Na Rundunar Yan Sandan Jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu Ya Baje-kolin Su Yau Alhamis. Daga Jamilu Dabawa, Katsina
Matafiya na shan wuyar sayen tikitin jirgin kasan Abuja-Kaduna ta intanet

Matafiya na shan wuyar sayen tikitin jirgin kasan Abuja-Kaduna ta intanet

Duk Labarai
Duk da shigo da tsarin sayan tikitin shiga jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ta intanet da gwamnatin Najeriya ta yi a shekarar 2021, har yanzu fasinjoji na shan dan karen wuya kafin samun shi. Tsohon ministan sufurin kasar Rotimi Amaechi ne ya fito da tsarin a zamanin mulkin tsohon shugaban kasar Muhammadu Buhari, da nufin magance cuwa-cuwar saida tikitin da ake zargin ma'aikatan wurin na yi. Gwamnatin Najeriya ta kashe naira miliyan 900 domin inganta hakan, sai dai bincike na baya-bayan nan da jaridar Solacebase ta fitar, ta raiwato a tashar jirgi ta Idu da Kubuwa a Abuja babban birnin kasar ya nuna bata sauya zani ba. Dubban matafiyan da a kowacce rana suka dogara da jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna na shan dan karen wuya kafin samun tikitin, ko dai dalilin rashinsa a intanet...
Najeriya ta ware biliyan 60 na ciyar da ƴan firamare a 2025

Najeriya ta ware biliyan 60 na ciyar da ƴan firamare a 2025

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ware naira biliyan 60 domin ciyar da 'yan makarantar firamare a sassa daban-daban na kasar a cikin kasafin kudin 2025. Za ai aikin ne karkashin shirin gwamnati na farfado da tattalin arziki wato Economic Recovery Growth Plan (ERGP). Jaraidar Dailty Trust ta tawaito cewa, kafin a sauya ministan ilimin kasar ya fara sanar da hakan wanda dama shirin ciyar da daliban yake karkashin ma'aikatarsa, kafin daga bisani a mayar da shi karkashin ofishin shugaban kasa. An ware wa ma'aikatar ilimi kudi naira biliyan 348, cikin sama da naira tiriliyan 2. 517, wanda hakan na daga cikin fannin da ya fi samun kaso mai tsoka a kasafin kudin, duk da bai kai adadin da Bankin Duniya ya bayar da shawara na kashi 20 zuwa 30 cikin 100 na kasafin kudin ba. Har wa yau, ma'aikatar il...