Friday, January 23
Shadow

Ba zamu amince da kari dan kadan ba akan Dubu 60>>NLC

Kungiyar Kwadago ta NLC ta bayyana cewa, ba zata amince da kari dan kadan, wanda bai kai ya kawo ba akan Naira Dubu 60 ba.

Kungiyar Kwadago ta NLC dai ta amince ta dakatar da yajin aikin da take dan bayar da dama ga gwamnati ta mata kari akan Naira Dubu 60 na mafi karancin Albashi.

Shugaban kungiyar Kwadago ta TUC, Festus Osifo ne ya bayyana haka a wata ganawa da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV.

Yace su basu nace wai sai an biyasu Naira Dubu dari hudu ba amma dai abinda suke cewa, shine a biyasu albashi me kyau.

Karanta Wannan  Kan mu ya daure, Bamu san wanne hukunci zamu yi amfani dashi ba>>Hukumar 'yansandan jihar Kano bayan da aka aika mata hukunce-hukuncen kotu har 5 da suka shafi masarautar Kano, saidai ta bayyana abinda zata yi nan gaba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *