Wednesday, March 18
Shadow

Buhari bai so Tinubu ya zama shugaban kasa ba>>Inji Dan Jarida Sam Omatseye

Dan Jarida, Sam Omatseye ya bayyana cewa, tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari bai so Tinubu ya zama ahugaban kasa ba.

Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi.

Yace tun a shekarar farko aka so a samu matsala tsakanin Buhari da Tinubu amma saboda Buharin na tunanin zarcewa, shiyasa ba’a yi fadan ba.

Yace cire tsohon gwamnan Edo, Adams Oshiomhole daga mukamin shugaban APC na daya daga cikin dabarun hana Bola Ahmad Tinubu zama shugaban kasa da Gwamnatin Buhari ta bijiro dasu.

Yace hakanan akwai wasu gwamnoni ma da basu so Tinubu ya zama shugaban kasa ba.

Karanta Wannan  Mace ta Gari: Mijina Ya Taba Hana Ni Zuwa Umarah A Lokacin Bai Fi Awanni Hudu Ya Rage Mu Tashi Ba, Amma Saboda Kauna Da Biyayya Haka Na Hakura, Inji Bahijja Kabara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *