![Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki](https://hutudole.com/wp-content/uploads/2024/06/18460643_nlcnigerialabourcongress1280x7201024x576_webpee2a90680ff75c8dfa41fe93b31604d7-780x440.webp)
Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki
Kungiyar Kwadago, NLC ta bayyana cewa bata akince da tayin Naira dubu 62 a matsayin mafi karancin Albashi ba.
Tace kai ko dubu 100 ba zata amince dashi a matsayin mafi karancin Albashin ba, Kungiyar tace wannan kudi sun yi kadan wa ma'aikata su rayu ciki rufin asiri.
Mataimakin babban sakataren kungiyar, Chris Onyeka ne ya bayyana haka a Channels TV yayin ganawa dashi ranar Litinin.
Ya kuma ce kwaki 7 ko sati daya da suka baiwa gwamnati kan ta bayyana matsayinta ya kare ranar Talata, kuma idan gwamnatin ta dage akan hakan, zasu sake zama ranar talatar dan tsayar da matsaya kan ci gaba da yajin aikin.
“Our position is very clear. We have never considered accepting N62,000 or any other wage that we know is below what we know is able to take Nigerian workers home. We will not nego...