Tuesday, December 17
Shadow

Siyasa

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Da Duminsa: Kungiyar Kwadago, NLC ta yi watsi da tayin Naira dubu suttin da biyu(62,000) ta bayyana ranar da zata ci gaba da yajin aiki

Siyasa
Kungiyar Kwadago, NLC ta bayyana cewa bata akince da tayin Naira dubu 62 a matsayin mafi karancin Albashi ba. Tace kai ko dubu 100 ba zata amince dashi a matsayin mafi karancin Albashin ba, Kungiyar tace wannan kudi sun yi kadan wa ma'aikata su rayu ciki rufin asiri. Mataimakin babban sakataren kungiyar, Chris Onyeka ne ya bayyana haka a Channels TV yayin ganawa dashi ranar Litinin. Ya kuma ce kwaki 7 ko sati daya da suka baiwa gwamnati kan ta bayyana matsayinta ya kare ranar Talata, kuma idan gwamnatin ta dage akan hakan, zasu sake zama ranar talatar dan tsayar da matsaya kan ci gaba da yajin aikin. “Our position is very clear. We have never considered accepting N62,000 or any other wage that we know is below what we know is able to take Nigerian workers home. We will not nego...
Kasar Rasha na takurawa ‘yan Afrika dake kasarta, ko dai su shiga aikin soja, su je yaki da Ukraine ko kuma ta dawo dasu gida

Kasar Rasha na takurawa ‘yan Afrika dake kasarta, ko dai su shiga aikin soja, su je yaki da Ukraine ko kuma ta dawo dasu gida

Siyasa
Rahotanni daga kasar Rasha na cewa, kasar na takurawa 'yan Afrika dake kasar shiga aikin soji dan yin yaki da kasar Ukraine. Rahoton jaridar Bloomberg ya bayyana cewa, kasar ta Rasha tana kuma takurawa hadda dalibai dake karatu a kasar. Saidai duk da haka wasu na baiwa jami'an tsaro cin hanci dan su kyalesu su zauna a kasar ba tare da su shiga aikin sojan ba ko kuma an dawo dasu gida ba. Yakin Rasha da Ukraine dai kullun sai kara kazancewa yake inda Ukraine din ke ci gaba da samun goyon bayan kasashen Yamma da Amurka.
Bai kamata Tinubu ya soki Gwamnatin Buhari ba saboda cewa yayi zai dora daga inda Buhari ya tsaya>>Buba Galadima

Bai kamata Tinubu ya soki Gwamnatin Buhari ba saboda cewa yayi zai dora daga inda Buhari ya tsaya>>Buba Galadima

Siyasa
Jigo a jam'iyyar NNPP, Injiniya Buba Galadima ya bayyana cewa, bai kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dorawa Buhari ko wane irin laifi ba. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a jaridar Sunnewsonline. Yace dalilin da yasa yace haka shine Tinubu yayi Alkawrin dorawa akan inda shugaba Buhari ya gama mulkinsa. Da aka tambayeshi ko me zai ce kan matsin rayuwar da ake ciki, Buba Galadima ya kada baki yace ai 'yan Najeriya ne suka siyowa kansu da kudinsu. Yace sai da ya gargadi mutane amma suka kiya.
Ji yanda ake ciki kan maganar mafi karancin Albashi tsakanin Gwamnati da NLC, inda ake tunanin za’a sake komawa yajin aiki

Ji yanda ake ciki kan maganar mafi karancin Albashi tsakanin Gwamnati da NLC, inda ake tunanin za’a sake komawa yajin aiki

Siyasa
Tattaunawa na ci gaba da gudana tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar kwadago ta NLC da TUC inda ake tsammanin za'a karkare a yau. Kungiyar tace ta gabatarwa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da bukatarta ta a biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin albashi kuma tana jiran ta ji amsa daga gareshi. Saidai matsayar gwamnati shine biyan Naira 62,000 a matsayin mafi karancin Albashin. Shuwagabanni kwadagon sun je Geneva, Kasar Switzerland inda suke halartar taro kan kungiyoyin kwadago na Duniya. Kuma ana tsammanin bayan aun kammala taron, zasu dawo a samu matsaya kan mafi karancin Albashin.
Suma Sanatoci Mafi karancin Albashi ya kamata a biyasu>>Inji Father Mbaka

Suma Sanatoci Mafi karancin Albashi ya kamata a biyasu>>Inji Father Mbaka

Siyasa
Babban malamin Kirista, Father Ejike Mbaka ya bayyana cewa, kamata yayi suma 'yan majalisar tarayya a rika biyansu mafi karancin Albashi. Ya bayyana cewa ma'aikata dakw ainahin wahala wajan aiki amma sune ake biya kudade 'yan kadan inda yace sam hakan bai dace ba. Yace a mayar da mafi karancin Albashin a rika biyan kowa dashi har 'yan majalisar kada a mayar da wasu bayi. Yace saboda menene za'a rika biyan 'yan majalisar Alawus wanda ya wuce ka'ida?
Mu fa har yanzu muna nan kan matsayin mu sai Gwamnati ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi>>NLC

Mu fa har yanzu muna nan kan matsayin mu sai Gwamnati ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi>>NLC

Siyasa
Kungiyar kwadago ta NLC ta jaddada matsayinta na cewa sai Gwamnatin tarayya ta biya Naira 250,000 a matsayin mafi karancin Albashi. Shugaban NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana haka a inda yace suna jiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauki mataki kan lamarin. Gwamnatin tarayya dai tace Naira 62,000 ne zata iya biya a matsayin mafi karancin Albashin. Saidai Gwamnoni sunce au bazama su iya biyan hakan ba idan dai ba duka kudaden da suke samu bane zasu rika biyan Albashi dashi ba. Yanzu dai abin jira a gani shine yanda zata kaya.
Masu zanga-zanga sun yi artabu da ƴan sandan Isra’ila

Masu zanga-zanga sun yi artabu da ƴan sandan Isra’ila

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Siyasa, Yakin gaza da isra'ila
Masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnati sun yi taho mu gama da ƴan sanda, a daidai lokacin da ake gangamin a sassan Isra'ila kan kiran a kuɓutar da sauran waɗanda ke hannun Hamas. Sai dai mai magana da yawun sojin ƙasar,Rear admiral Daniel Hagari ya ce su na ƙoƙari kan batun. Ya ce dakarun Isra'ila sun ɗauki makwanni su na shirye-shiryen aikin nan, an ba su horo kan yadda za su kuɓutar da mutanenmu, ba za mu gaji ba har sai sauran sun dawo. Masu zanga-zangar su na sukar firaiminista Benjamin Netanyahu, wanda ke ganawa da iyalan waɗanda aka saka maimakon waɗanda ke cikin tashin hankali da rashin tabbacin ko nasu ƴan uwan za su dawo gida a raye.
NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi da aka shigar da su Najeriya daga India

NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi da aka shigar da su Najeriya daga India

Siyasa
Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Najeriya, NDLEA ta ce jami'an ta sun kama kwalba 175,000 ta miyagun ƙwayoyi da maganin tari da aka shigar da su ƙasar daga India. Kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya ce sun yi wannan nasarar ne mako guda bayan wata irin ta da suka samu, inda suka kama hodar ibilis da aka shiga da ita Najeriyar, a jihar Rivers. Ya yi bayanin cewa NDLEA da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro ta yi nasarar kama kayan laifin ne a ranar juma'a, 7 ga watan Yunin bana, bayan sun nemi gudanar da cikakken bincike a kan kayan da aka shigo dasu daga ƙasashen waje. Babafemi ya kuma bayyana cewa akwai sauran kayan laifi da suka haɗa ga kƙwaya da tabar wiwi da hodar ibilis da jami'an NDLEA suka kama a sassan Najeriya, a cikin makon da ya gabata. Ya ce daga cikin ...
Babbar Sallah: Gwamnatin jihar Sokoto ta amince a biya albashin watan Yuni

Babbar Sallah: Gwamnatin jihar Sokoto ta amince a biya albashin watan Yuni

Siyasa, Sokoto
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya amince a biya albashin watan Yuni ga ma'aikatan jihar daga ranar Litinin. Gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne domin bai wa ma'aikatan gwamnatin jihar damar yin bikin babbar sallah cikin walwala. Sakataren yaɗa labaran gwamnan Sokoto, Abubakar Bawa, ya ce dukkan ma'aikatan jihar, da na ƙananan hukumomi da kuma ƴan fansho ne za su amfana da wannan karamci. Abubakar Bawa, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na ci gaba da biyan albashin ma'aikata a kan lokaci, kamar yadda ya ce ya zama al'adar gwamantin, biyan albashi a ranar 20 zuwa 21 na kowanne wata, tun bayan karɓar ragamar mulki. Dama dai gwamnonin jihohin Arewa sun saba yin irin wannan karamci idan aka samu yanayi na gudanar da shagulgulan sallah amma wata bai ƙare ba.
Gwamna Buni Ya Yi Watsi Da ‘Yancin Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi

Gwamna Buni Ya Yi Watsi Da ‘Yancin Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi

labaran jihar yobe state, Siyasa
Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya yi watsi da matakin bai wa kananan hukumomin kasar ‘yancin cin gashin kansu. Buni ya bayyana ra’ayinsa ne jim kadan bayan kada kuri’arsa a zaben kananan hukumomi a mazabar sa da ke Buni Gari. “Lokacin da na hau mulki a shekarar 2019, tunanina shi ne in ba kananan hukumomi cin gashin kai. Sai dai abin takaici shi ne kananan hukumomi shida cikin 17 na jihar Yobe ba sa iya biyan ma’aikata albashi. “Saboda haka, hikimar da ke tattare da wannan asusun hadin gwiwa, wanda ya hada da kokarin kananan hukumomi tare da jihar tare da hadin gwiwa wajen aiwatar da wasu ayyuka, ra’ayi ne da aka samu daga wadannan gazawar,” in ji shi. Gwamnan ya kuma bayyana fatansa game da makomar cin gashin kan kananan hukumomi a Najeriya. "Dimokradiyyarmu tana girma,...