Friday, March 27
Shadow

Da Duminsa: An bayyana halin da Sheikh Khalifa Sani Zaria ke ciki

Biyo bayan rade-radin da ake ta yayatawa cewa Babban Malamin Addinin Islama dake tsare a hannun Hukumomin Najeriya, Sheikh Khalifa Sani Zaria ya rasu.

Rahotanni daga PRNigeria sun tabbatar da cewa malam yana nan da ransa bai rasu ba.

Wata majiya daga Hukumar ta DSS ce ta bayyanawa PRNigeria hakan inda tace malam nanan Hukumomin soji dana DSS na masa tambayoyi.

Ana zargin Malam da karbar Naira Miliyan 2 ne dan yiwa sojan dake shirin yiwa shugaba Tinubu juyin Mulki Addu’a, saidai iyalan malam sun karyata wannan zargi.

Karanta Wannan  ADC ta zargi APC da shirin tafka maguɗi a zaɓen cike gurbi na Kaduna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *