
Hukumar yaki da Rashawa da cin hanci EFCC ta bayyana cewa tana tsare da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Tace a hannunta zai kwana ana masa tambayoyi.
Wata majiya daga EFCC din ce ta bayyanawa jaridar TheCable hakan.
Majiyar tace watakila a saki Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ranar Talata idan aka kammala yi masa tambayoyi.