
Shugaban kamfanin NNPCL, Bayo Ojulari ya bayyana cewa, Rayuwarsa data sauran ma’aikatan kamfanin na cikin hadari.
Yace ana barazanar saukeshi daga kan mukaminsa, inda yace laifinsa kawai shine kyaran da ya kawo a harkar mai a kasarnan kamar yanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi umarni.
Ya bayyana hakane a Abuja yayin da kungiyar ma’aikatan man, PENGASSAN ta kai masa ziyara bisa jagorancin shugabanta, Comrade Festus Osifo.
Yace suna kokarin ganin an gyara matatun man fetur din Najeriya sun dawo aiki yanda ya kamata.