Friday, July 17
Shadow

Na ji dadin Dawowa Najeriya, Kuma ina gina sabuwar Najeriya fil>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, ya ji dadin dawowa Najeriya daga ziyarar da ya kai kasashen Japan da Brazil.

Shugaba Tinubu ya bayyana hakane ta shafinsa na sada zumunta inda yace daya daga cikin aikin da ‘yan Najeriya suka bashi a shekarar 2023 shine na kulla hadaka da kasashen Duniya dan kawo ci gaba.

Shugaban yace a ziyarar da ya kai kasashen Brazil da Japan Najeriya ta kulla yarjejeniya da kasashen a fannonin kudi, sufuri, kimiyya da fasaha da sauransu.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Gwamnan Kaduna ya baiwa malaman Addinin Islama da suka taimaka masa yaci zabe kyautar Tsabar Naira Miliyan 10

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *