Friday, December 26
Shadow

Da Duminsa: Naji Dadin Abinda sojan Ruwa, Yerima yawa Ministan Abuja, Wike, yayi daidai, kuma zan tabbatar babu abinda ya samu sojan>>Inji Ministan Tsaro, Muhammad Badaru

Ministan Tsaro, Muhammad Badaru ya bayyana goyon bayansa ga Matashin soja da ya tare Ministan Abuja, Nyesom Wike ya hanashi shiga wani fili a Abujan.

Minista Badaru yace suna goyon bayan abinda Sojan yayi kuma sun jinjina masa sannan zasu bashi kariya saboda yana bakin aikinsa ne.

Badaru yace zasu ci gaba da baiwa kowane soja Kariya da goyon baya muddin ya tsaya tsayin daka a bakin aikinsa.

Hakan na zuwane bayan da a wajan rikicin ma sai da Wike ya kira shugaban sojoji, CDS.

Karanta Wannan  Bidiyo Da Duminsa: Hukumomin Gwamnatin Soji ta kasar Burkina Faso sun ce auna rike da sojojin Najeriya 11 bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa a kasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *