
Dan majalisar wakilai, Leke Abejide wanda dan jam’iyyar ADC ne ya maka shuwagabannin jam’iyyar na riko David Mark, da Rauf Aregbesola a kotu inda yace kotu ta saukesu.
Hakan na zuwane a yayin da ake tsaka da fama da rikicin Nafiu Bala.
Ya shigar da karar ne a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja inda kotun ta tsayar da ranar 13 ga watan Afrilu dan yanke hukunci.
Jam’iyyar ADC na fuskantar kalubale kala-kala inda take zargin hannun APC a lamarin.