Friday, January 16
Shadow

Da Duminsa:An kama Omoyele Sowore a babban kotun tarayya dake Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘Yansanda a babban birnin tarayya, Abuja sun kama dan fafutuka kuma me rajin kare hakin bil’dama, Omoyele Sowore.

An kamashi ne a yayin da yake fitowa daga cikin babbar kotun tarayya dake Abuja inda akewa Nnamdi Kanu shari’a.

Rahoton yace ‘Yansandan sun saka Sowore a gaba yayin da yake fitowa daga Kotun inda suka ce su wuce office.

Bayan da aka yi tirka-tirka Sowore dai ya yadda an tafi dashi.

Wani na kusa da Sowore yace dama can ‘yansandan sun gayyaceshi amma Azarbabin sune yasa suka zo kamashi.

Karanta Wannan  Majalisar Jihar Kano ta ce tana goyon bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma APC hakanan kuma suma zasu bishi zuwa APC din

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *