Wednesday, April 8
Shadow

Da Duminsa:An kama Omoyele Sowore a babban kotun tarayya dake Abuja

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘Yansanda a babban birnin tarayya, Abuja sun kama dan fafutuka kuma me rajin kare hakin bil’dama, Omoyele Sowore.

An kamashi ne a yayin da yake fitowa daga cikin babbar kotun tarayya dake Abuja inda akewa Nnamdi Kanu shari’a.

Rahoton yace ‘Yansandan sun saka Sowore a gaba yayin da yake fitowa daga Kotun inda suka ce su wuce office.

Bayan da aka yi tirka-tirka Sowore dai ya yadda an tafi dashi.

Wani na kusa da Sowore yace dama can ‘yansandan sun gayyaceshi amma Azarbabin sune yasa suka zo kamashi.

Karanta Wannan  Allah Sarki: 'Yan Tàwàyèn Hòùthì daga kasar Yèmèn sun zama na farko a Duniya da suka goyi bayan Ìràn ba da baki ba, yanzu haka sun cillawa Israyla makami kuma Israylan ta kasa tareshi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *