Wednesday, February 25
Shadow

Da gangan wasu mugayen ‘yan Najeriya ke kara farashin kaya dan kawai su bata min suna>>Gwamnatin Tinubu

Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa da gangan wasu ‘yan Najeriyar ke karawa kayan da suke sayarwa farashi dan kawai su batawa gwamnatinsa suna.

Hadimin shugaban kasar me bashi shawara akan tattalin arziki, Tope Fasua ne ya bayyana hakan.

Yace banda alkaluma tattalin arziki, akwai sauran abubuwan da ke sanya farashin kayan masarufi su tashi a Najeriya, hadda muguntar wasu ‘yan kasar.

Ya bayyana hakane a shafinsa na Facebook yayin da yake martani ga wani rahoto dake cewa wani gidan mai yana biyan ma’aikatansa Naira Dubu 10.

Karanta Wannan  Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana'a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *