Sunday, December 14
Shadow

Da gangan wasu mugayen ‘yan Najeriya ke kara farashin kaya dan kawai su bata min suna>>Gwamnatin Tinubu

Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa da gangan wasu ‘yan Najeriyar ke karawa kayan da suke sayarwa farashi dan kawai su batawa gwamnatinsa suna.

Hadimin shugaban kasar me bashi shawara akan tattalin arziki, Tope Fasua ne ya bayyana hakan.

Yace banda alkaluma tattalin arziki, akwai sauran abubuwan da ke sanya farashin kayan masarufi su tashi a Najeriya, hadda muguntar wasu ‘yan kasar.

Ya bayyana hakane a shafinsa na Facebook yayin da yake martani ga wani rahoto dake cewa wani gidan mai yana biyan ma’aikatansa Naira Dubu 10.

Karanta Wannan  Kalli yanda wani direba ya dauki dansanda a Arewa Bidiyo yayin da dansandan ke cewa sai ya bashi cin hancin Dubu biyu, shi kuma yace dubu daya zai bayar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *