Friday, December 5
Shadow

Da na so zama shugaban kasa a karo na 3, nasan yanda zan yi in samu, babu wanda ya isa ya hanani>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya karyata rade-radin dake yawo cewa ya so ya sake zama shugaban Najeriya a karo na 3.

Obasanjo ya bayyana hakane a wajan wani taro kan Dimokradiyya da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya shirya.

Yace babu wanda zai iya cewa ya kirashi ya gaya mai cewa yana son zarcewa a karo na 3 akan mulki.

Yace neman a yafewa Najeriya bashin da ake binta da yayi a zamanin mulkinsa, yafi neman zama shugaban kasa a karo na 3 wahala.

Karanta Wannan  Na Yafe Duk Wata Rashin Fahimta Da Ta Shiga Tsakanina Da Marigayi Sheik Idris Dutsen Tanshi, Inji Gwamna Bala Mohammed yayin da yaje ta'aziyyar malamin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *