Friday, January 16
Shadow

Dalibai Kiristoci na Jami’o’in Federal University Kashere, Gombe da BUK Kano sun koka da cewa akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya

Daliban jami’o’in Federal University Kashere, Gombe dana jami’ar BUK, Kano Kiristoci sun koka da cewa, akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya.

Daya daga cikin daliban na Kashere ne ya fito yake zanga-zanga shi kadai inda yace suna bukatar Coci a jami’ar.

Wani kirista ta bayyana cewa abin haushin shine jihar Gombe da yawan musulmai da kirista daidai suke watau 50/50 amma irin wannan abin na faruwa.

Karanta Wannan  Kwana daya bayan da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya jinjinawa Gwamnatin Tinubu bisa farfado da tattalin arzikin Najeriya, Bankin Duniya yace duk da kokarin Gwamnati na farfado da tattalin arzikin, Mutane Miliyan 139 ne suka tsunduma cikin bakin Talauci a Najeriya

Wannan zanga-zanga da dalibin yayi tasa shima wani dalibin jami’ar BUK Kano ya bayyana cewa suna hakan take, akwai masallatai a BUK amma su ba’a basu damar gina coci ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *