Thursday, April 24
Shadow

Dan Allah ku gayawa El-Rufai ya shafa min Lafiya, Ni Aiki nane a gabana ba cece-kuce a gidajen watsa labarai ba>>Nuhu Ribadu

Ba Zan Yi Musayar Yawu Da Nasir El-Rufai Ba, Cewar Nuhu Ribadu

“An ja hankalina zuwa ga hirar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya yi da kafar yada labarai da yammacin ranar Litinin.

Da ba don gudun kada na yi shiru a gaskata maganganunsa ba, da na yi watsi da shi. Saboda na fi shagaltuwa da tarin aiyukan da ke gabana,fiye da tanka ire-iren su Nasir El-Rufai a kafafen yada labarai.

Duk da cin zarafi da aibata ni da Nasiru yake yi, hakan bai sa na taba fadin wani mummunan abu akansa ba a ko’ina. Ba don komai na ki aibata shi ba sai don mutunta zumuncin da ke tsakaninmu da kuma abotar mu ta baya, don haka abinda ban yi tun a baya ba, ba zan fara yanzu ba.

Karanta Wannan  Kasar Amurka ta ki yadda ta bayar da bayanai akan rayuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda tace wakilintane dake taimaka mata wajan cimma burikanta

Sai dai ina kira ga jama’a da su yi watsi da ikirarin El-rufai akaina

Bari na kankare muku shakku in fadi da babbar murya cewa ban taba tattauna batun ko zan yi takarar shugabancin kasa a shekarar 2031 da kowa ba, domin hankalina da gangar jikina sun ta’allaka ga aikina na ganin ci gaban Najeriya da nasarar gwamnatin shugaba Tinubu.

Don haka ina rokon Nasir El-Rufai da ya bar ni na ci gaba da fuskantar aikina na gina kasa kamar yadda ban dame kaina da al’amuransa ba”. Nuhu Ribadu

Me zaku ce ?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *