Wednesday, March 25
Shadow

Dan jarida ya zargi hukumar Kwastam da taimakawa masu fasa kwaurin shikafa zuwa cikin Najeriya

Dan jarida me binciken kwakwaf, Fisayo Soyombo ya zargi hukumar Kwastam da taimakawa masu fasa kwaurin shinkafa zuwa cikin Najeriya.

A bayanan da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya ce yanzu haka ana sauke shinkafar da aka shigo da ita daga kasar Benin Republic a Lusada dake karamar hukumar Ado Odo/Ota ta jihar Ogun.

Soyombo ya bayyana cewa lamarin na faruwane a ranar Laraba inda yace kuma an sallami duka wani jami’in Kwastam da zai kawo tangarda a lamarin.

Dan jaridar yace sauran shinkafar za’a tafi da ita zuwa Legas.

A baya dama dan jaridar ya bayar da bayanai akan shigowa da shinkafar amma hukumar kwastam ta karyatashi.

Karanta Wannan  Hadisi ya tabbatar da cewa, Ceton Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) akan masu aikata manyan zunubaine, shiyasa nace ina son in shiga Aljannah ba da ceton Annabi ba>>Dr. Hussain Kano

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *