
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, dolene gwamnati ta zage ta magance matsalar tsaro idan tana son masu zuba hannun jari su shigo Najeriya.
Shugaban ya bayar da tabbacin Gwamnati na kwato garuruwan dake hannun ‘yan ta’adda musamman a Arewa maso gabas.
Shugaban ya bayyana hakane yayin ganawa da dattawa jihar ta Katsina a ziyarar da ya kai jihar inda yayi Alwashin yin amfani da na’urorin zamani da sauran kayan aiki na zamani dan magance matsalar garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro.
Shugaban yace babu ‘yan kasuwar da zasu je inda babu tsaro su zuba hannun jari, dan haka yace zasu hada hannu da gwamnatoci a kowane matakai su magance matsalar.