Sunday, December 14
Shadow

Gidajen Sayar da Man Fetur kusan Dubu biya sun kulle saboda rashin tabbas na farashi da yawaitar rage farashin da Dangote yake

Rahotanni sun ce gidajen saye d man fetur akalla 4900 ne suka kulle a fadin kasarnan saboda rashin tabbas na kasuwar man fetur din.

‘Yan kasuwar da yawa basa iya sayen tankar mai, inda a yanzu sai ka da an hada kudi na ‘yan kasuwa biyu zuwa uku kamin su samu damar sayen tankar man fetur daya wadda a baya cikin sauki mutum daya ke iya sayenta.

Daga watan Janairu na shekarar 2025 zuwa Afrilu matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin ta sau 6 inda ya fara a Naira 950 har ya sakko zuwa 835.

‘Yan kasuwar da basu ma da kudin da za’a yi wannan hadaka dasu dole tasa sun rufe gidajen man fetur din.

Karanta Wannan  Munin Tattalin arzikin Najeriya a yanzu yafi na lokacin da aka baiwa Najeriya 'yanci a shekarar 1960>>Inji Shugaba Bankin Afrika

Bayan zuwan Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, Ta cire tallafin man fetur wanda hakan yasa farashin ya koma hannun ‘yan kasuwa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *