
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, Gwamnatin Tarayya ta masa alkawarin bashi jirgin ruwan danyen mai guda 15 a wata.
Yace amma bata cika wannan alkawari ba, Jirage 5 kawai take bashi a wata.
Dangote ya nemi Gwamnatin data cika Alkawarin data daukar masa.
Yace matatarsa na fitar da gangar tataccen man fetur 650,000 a kullun kuma yana biyawa Najeriya dama Afrika bukatar man fetur dinsu