Thursday, December 25
Shadow

Gwamnatin tarayya zata baiwa ‘yan Najeriya Miliuan 8.8 tallafi dan rage musu radadin talauci, ji yanda za’a yi rabon

Gwamnatin tarayya ta bayyana aniyarta ta rabawa ‘yan Najeriya Miliyan 8.8 tallafi dan rage musu radadin talauci.

Gwamnatin tace zata raba wannan tallafi ne a mazabun dakw fadin kasarnan da suka kai 8,809.

A ranar Alhamis ne gwamnatin ta sanar da wannan shiri sannan tace za’a gudanar dashi ne a karkashin ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki.

Gwamnatin tarayyar tace, Kungiyar bayar da lamuni ta Duniya, IMF ta karfafa mata gwiwa wajan aiwatar da wannan aiki.

Karanta Wannan  Sanata Natasha Ta Ci Karo Da Hoton Wannan Mutumin Ne Dauke Da Hular Da Aka Rubuta Sunanta A Jiki, Ganin Yadda Mutumin Ya Yi Kalar Tausayi, Hakan Ya Sa Ta Sa Aka Nemo Shi Ta Ba Shi Wani Kunshi Na Kudi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *