Wednesday, May 14
Shadow

Gwamnatin tarayya zata ranto Naira Tiriliyan 6.6 dan cike gibin Kasafin kudi

Rahotanni sun bayyana cewa, akwai yiyuwar Gwamnatin tarayya zata ranto Naira Tiriliyan 6.6 dan cike gibin kasafin kudi.

Gwamnatin zata ciwo bashinne a wannan shekarar ta 2024 kuma zata yi hakan ne dan samar da kudin da zata biya tallafin man fetur wanda zai lakume Naira Tiriliyan 5.4.

Kafar yada labarai ta Reuters ce ta ruwaito wannan labari.

Saidai Gwamnatin tarayya ta ci gaba da nanata cewa ita fa har yanzu bata biyan tallafin man fetur.

Karanta Wannan  Kwamishinan kananan hukumomi na jihar Bauchi Ahmad Jalam ya rasu sakamakon wani hatsarin mota da ya ritsa da shi a kan hanyar Misau-Darazo ranar Asabar a cewar gwamnatin jihar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *