
Kungiyar kwadago ta NLC ta bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu hankalinshi ba aka ‘yan Najeriya dake fama da wahala ake ba, yana kan yanda zai sake cin zabene.
Shugaban kungiyar, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a wajan wani taro a Akwa-Ibom.
Yace gwamnatocin jihohi dana tarayya suna yiwa ma’ikata sata ta hanyar hanasu hakkokinsu.
Sannan ya koka da take ‘yancin fadar Albarkacin baki da yace gwanati na yi.